SIRRIN HAJARA




DAYA

R
okon da nake a wurin Allah, nan a duniya har  can a lahira Allah sa muga annabi Muhammadu!
Wadannan wasu jerin gwanon baituka ne daga cikin wata wakar shahararren shudadden mawakin nan mamman shata, suke tashi a hankali a gaban motar da muke ciki. A radiyon motar da watakila ya shafe shekara talatin yana shan duniya! Koda yake ba zan sa watakila ba saboda idan kiyasi zanyi da iya tunanina zan iya rantsewa ya kai shekara tamanin saboda yanzu na tabbata ma babu irin wannan samfurin akwatin radiyon a duniya. Ba radiyon bace kadai tsohuwa hatta motar da muke ciki da take tafe kamar zata hantsila idan muka hau gangara da tudu ta shafe sama da shekaru a duniya. Ni ba wannan ne ya dame ni ba, abunda ya dame ni kawai shine kallace kallace na dan ina taso in kalli yadda na tafi na dawo na tarar da kauyen namu.
         Yana nan bai can za ba, duk da cikin dare ne amma farin wata ya haskaka komai. tun daga kan hanya nake gane hakan, saboda ban ga wani sauyi da ya yi yawan da zai sa in fahimci wani abu ya sauya daga tsarin kauyen ba, musamman ma da yake da rani na tafi na bar kauyen, yanzu haka ma da rani na dawo dan haka shi yasa ban ga wani sauyi ba koda kuwa na shuka ne
         Motar ta tsaya a hankali a karkashin wata darbejiya mai yawan ganyayyaki inda nan ne yake zama tashar ‘yan kauyen mu idan sun hau mota daga inda muka hau wato kauyen magaji. Direban ya wage murya da karfi yadda kowa zai ji ya fara sanarwa.
“Wadanda zasu sauka a kauyen TSAUNIN MARKE an kawo, sai su yi hanzarin sauka dan muna sauri dare ne, muna so mu wuce”
Na kimkimi jakata ta baya irin ta ‘yan birni saboda ko ba komai na je birni na yi shekara daya can dan haka ina da tabbacin na waye, ba tare da jiran komai ba na nufi hanyar da zata sada ni da cikin kauyen namu daga shararriyar hanyar da motar ta ajiye ni, saboda tun kafin mota ta taso daga kauyen magaji ake amsar kudin kowa, na juya kadan dan naga ko akwai wanda zai sauka sai na ga babu, harma motar ta fara tafiya a hankali cikin kakarin ihun ta na tsufa da neman agajin hutawa
Ban damu ba na ci gaba da tafiya ta, na duba agogon dake hannuna naga karfe daya da rabi da minti takwas na dare, na girgiza kai ina gyara jakata dake wuya na, na tabbata sai na ba mutanen gida mamaki, yadda nayo tafiyar dare haka da ban saba da ita ba
Ko kuma su, zasu bani mamaki

Na dan yi nisa kenan kafin na karasa cikin kauyen da yake akwai ‘yar tafiya ta tazarar da ba zata wuce minti biyar ba. Haka kawai na daga kai na kalli gefena na hagu kamar an dasa ni na tsaya ina kallon ikon Allah, ina kallon wata doguwar mata mai dogayen kaya ta nufo hanyar da nake a hankali, gabana ya so ya fadi saboda ba a kan hanya na ganta ba, ta cikin jeji na ga tana tahowa, sanyin da kafafuna suka yi yasa na dan jinkirta kamar mai jarumta, ta ratso ta cikin farin watan a cikin talatainin daren ta nufo ni, ganin wurina tayo a hankali ya halittawa zuciyata tsoro mai yawa sosai, na kasa motsawa ina jiran inji ar! In yanka da gudu, doguwa mai dogayen fararen kaya ta nufo ni bata daina ba, kamar yadda zuciyata bata daina luguden tsorata ba, ta karaso daf da ni a yananyin ta gaba daya babu tsoro sai dai akwai hawaye a tare da ita, ta dan tsaya tana kallo na kamar yadda nake kallonta, sannan a hankali na kai kallona kan kafarta da niyyar ko zanga kofato in yanka a guje, sai nayi arba da wata siririyar kafa mai kyau da zubin yatsu masu tsayi masu kyawun gani.
A lokacin na tabbata idan da za’a tsarga fatata bana tsammanin za a samu jini na kai kawo, saboda yadda na ke cikin rudani.
Ta girgiza kai kawai ta juya ta kalli hanyar da na fito da niyyar tafiya, ba tare da tayi min maganar ba kuma na ga ta juya din. Gani ni kuma Allah yayi ni da matukar son jin kwakwaf! Da shegen son gulma, hakan yasa na daga murya a hankali nayi mata magana
“Baiwar Allah daga ina kike?”
Ta juyo a hankali kamar sitiyarin mota da fararen dogayen kayan dake jikinta ta kalle ni kana ta sake juyawa har yanzu bata yi min magana ba, da niyyar zata wuce, ni kuma na riga na kwadaitu da son jin daga inda take ko yaya ne, tunda dai na tabbata ba aljana bace, dan da aljanace da naga kofato!  Dan haka sai na sake tambayar ta karo na biyu
“Baiwar Allah daga ina kike, kuma ina zaki je?”
Ta sake juyowa tana kallona, gabana ya fadi ina ganin kamar da zarar ta juyo zan ga ta juyo min da kan kura ko damisa ne! amma da kanta ta juyo da kyakkyawar fuskar ta ta girgiza min kai, kana ta yi min magana a hankali da siririyar muryar ta
“Daga duniya nake, kuma cikin duniya zani, ko akwai inda ake zuwa bayan duniya?”
Na hadiye miyau dakyar kana na girgiza kai
“Babu, sai dai bayan nan akwai lahira”
“To can zani”
“Lahirar?”
“Ko zaka hana ne?”
Na yi sauri na girgiza kai tare da kauda kai yadda naga ta zaro min idanu, kana na ji tayi wani dogon tsaki kana ta juya tana surutu “mutane sai shegiyar tambaya kamar a gaban alkali, to ka biyo ni kaga inda zanje”

Na girgiza kai tare da sauke numfashi ina tunanin ina ni ina bin wannan doguwa mai dogayen kaya haka, bayan naji inda kika ambata? Koda bata ambaci lahira ba ba binta zanyi ba, gida na nufa, ina kallonta ta cikin farin watan tana ta tafiyar ta har tayi nisa ta haye titi ta nausa cikin daji inda na tabbata akwai matsala koda da ranane balle da cikin wannan uban dare, na juya na ci gaba da tafiya ta ina tunanin watakila lahirar zata je da gaske, watakila neman mutuwa take saboda wani bakin ciki da aka sata tunda ga hawaye nan a fuskar ta.
Na tabbatar shi kenan ni da ita mun rabu ba zamu sake haduwa ba dan haka bari in cire tunanin ta a raina.

watakila yanzu na fara ganinta

         Haka na mike ina ta tafiya ta har na shigo cikin kauyen, ina shiga na tarar da shagon na’ago a bude kamar yadda na tabbatar a bude zan ganshi, saboda sama da shekara goma shagon shi a bude yake kwana, da yake a jikin dakin sa yake kuma shi gashi gwauro wanda bai taba dandana aure ba, tun zamanin iyayen mu suna ‘yan yara har ya zuwa yanzu haka na’ago yake rayuwa shi kadai abunsa, na yi masa sallama. Na’agoya dago ya kalle ni kana ya dauke kai abinsa ya sake ci gaba da murza shaken da yake murzawa na gwangwani, ina tunanin shi har yanzu bai daina shaken nan ba, na zauna tare da sauke numfashi ina washe baki da tsammanin ganin sa ya nuna mamakin gani na da wannan dare, amma cike da mamaki yanayin sa gaba daya bai nuna haka ba, kamar wanda muke tare tun dazu naje na zaga na dawo haka ya kalle ni, na daure na yi masa magana
         “Na’ago mai kwanan  shago!  Ya baka nuna mamakin ganina cikin wannan talatainin daren bane?”
         Na ago ya yi tsaki tare da shakar shaken sa kamar babur din da ta saba da shake!
         “Aikin banza wai giwa ta ga shaho na shawagi” yaci gaba da shakensa tare da tari kamar mai ciwon taba! Yanda kasan dole! Haka yake shan wannan shake yayi ta tari kuma kullum sai yayi kwalla bayan ya gama shaken, “Yanzu fa baka fi minti talatin da barin nan ba, kuma sai inyi mamaki bayan ba tafiya kayi ta shekara goma ba”
         Nayi kasake ina kallon sa koda yake nasan halin na’ago da ban dariya hakan yasa na fashe da dariya ina mamakin yadda har yanzu bai bar shakiyancin sa ba, ya kalle ni kawai yana ganin kamar na tabu.
         “Ya kake yi min irin wannan ihun cikin dare haka ko ko so kake ‘yan doka suzo su kama ni?”
         “Ni ba ihu nake ba, dariya ce malam na’ago, naji ne ka ce wai ban fi minti talatin da barin nan ba, shine na ke dariya dan nasan ba haka bane”
         “Hmm! ku dai yaran zamani da son kure tsoffi! To ai koda na yi kari a kai ba zai wuce na minti goma ba, dan dai baka fi minti goma sha biyar da barin  shagon nan ba, ko kana nufin ba kai bane kace zaka je dauko tarkon ka da ka sa na zomo?”
         Na dan nutsu ina kallon malam na’ago yadda yake ta zuba haka kamar indararo kamar kuma yanayin sa da gaske yake, na sha mur dan yin magana da gaske
         “Haba malam na’ago, me yasa kake irin wannan maganar, ni yaushe na zo nan? Yanzu fa dawowa ta daga kaduna kenan, birni inda na tafi shekarar data wuce da rani”
Ya dakata da jujjuya shaken sa da yake yi ya kalle ni da kallon mamaki da hasala. Hawayen shaken da yake yi cike a idanunsa
         “Ka tashi ka tafi ka bani wuri tunda kai ma ka zama shashasha irin su mani mani, yaya zaka same ni dattijo kamata kayi ta min wannan zubar? Ko an gaya maka hankali na ya fara kaucewa ne, dazu fa ka wuce kayi yamma kana cewa zaka je ka dubo tarkon  zomon ka. Yaya kuma zaka zo ka rika ce min yanzu ka dawo kai aljani ne to?”
         Tabbas da gaske yake, yadda naga ya hakikice yana ta magana da tada jijiyar wuya na kalle shi sannan na kalli zoben hajara dake hannuna wanda dazu da rana da zamu rabu a kaduna take kuka ta bani tare da tabbatar min da in rike mata alkawarin soyayyarta. Amma gashi yanzu malam na’ago ya takarkare yana ta so ya maida ni wani mutum biyu!  
         “Ni fa da gaske nake malam na’ago kuma gaskiya bazan boye maka ba, kana so ka bani tsoro wallahi, yaushe ka ganni? Ni da nayi tafiya shekara daya bana gida, yanzu da dawowata kace ka ga na wuce...      .........?”
         Zai daga min hannu tare da daka min tsawa! Na san shi da masifa musamman idan yana da gaskiya, “Ko dai ka sha tiramol yayi maka yawa ne jamilu?”
         “Ai kaima kasan ina daya daga cikin yaran da basa shan komai a kauyen nan na ‘ago”
         “To ai shine nake tunanin ko ka fara shane, kasan sabon shiga yafi buguwa, idan ba haka ba yaya zaka zo kace min ba kai bane?”
         “Ko dai shaken da kake sha yau mai nauyi ne na’ago?”
         Ni da kaina nasan bai kamata in fada masa haka ba, saboda masifaffe ne ko ba haka bama, ya haife ni, ya zaro idanu yana kallo na kana ya kwashe da dariya
         “Ka ganni nan! Tun da nake babu wani kayan maye da ya taba kauda min tunani na dai dai da dakika daya, nasha banju na nasha wiwi, nasha taba, nasha sukudayi, nasha make uba, nasha garkami, nasha kafso, kai in tabbatar maka a zamanin sarki sulaimanu mai madaci har giya nasha a ranar bikin dakin sarautar sa, dan haka na fi gaban nan, nafi gaban kace wannan dan karamin abun alhakin ya kauda min tunani na”     
         Na yi kasake ina kallon sa¸ lokaci daya ya birkide kamar an aiko masa da sakon mutuwa, koda yake nasan baya son ana karyata shi duk da akwai shi da shegiyar karya, na mike tare da daukar jakata, dan na gaji da jin wannan tatsuniyar tashi ta almara, na kalle shi ina fita daga cikin shagon nashi
         “Kayi hakuri malam na’ago dama wasa nake yi maka”
         Ina jin shi daga can ciki yana min magana cike da ihu da masifa
         “Dama na san ni zaka rainawa wayau! Lallai kaima ka shiga jerin wadanda zanci ubansu a kwanakin nan! kada kaga dan kana ANGO!!
         Kalaman sa na karshe su suka iso kunne na da karfi, sune kuma suka sa na tabbatar da na’ago ya sha shaken da ya taba kwakwalwar sa yau, da yake halin tsufa
         “Kada kaga dan kana ango!”
Kalaman suka sake zuwa cikin kwakwalwata sune kuma suka sani dariya har lokacin da na karaso kusa da kofar gidan babana inda naga taron matasa sun kunna wuta da gungume icce suna gasa wasu kaji kamar yadda ake yi idan anyi biki a kauyen, na yi murmushi amma har lokacin dariyar malam na’ago bata barni ba, ina mamakin yadda tsoho kamar wannan yaki ya bar shake, lallai kuwa kwanan nan shake yana gaf! Da shake kwakwalwar sa ya daina ganewa gaba daya, ina karasowa daya daga cikin abokaina wato janaidu ya mike da sauri tare da goge kwallar hayakin da ke fuskar sa ya kalle ni a dan hasale da fushi
         “kai dan ka rainawa mutane hankali muna gasa kajin nan amma sai ka wani kinkimi jaka ka tafi neman zomo, to yanzu so kake kace mana ka kamo zomon?”
         Cak! Numfashi na ya nemi daukewa, meke faruwa ne? na fara nazari akan haka,  kalaman janaidu naji suna so suyi kama da kalaman malam na’ago

         ” dazu fa ka wuce kayi yamma kana cewa zaka je ka dubo tarkon zomon ka. Yaya kuma zaka zo ka rika ce min yanzu ka dawo kai aljani ne to?”

         Na tuno kalaman na’ago sannan yanzu ga abunda janaidu yake fada min
        
“kai dan ka rainawa mutane hankali muna gasa kajin nan amma sai ka wani kinkimi jaka ka tafi neman zomo, to yanzu so kake kace mana ka kamo zomon?”
         Nayi shiru ina kallon sa. Ina mamaki, mamaki sosai. Ba haka ya kamata su tare ni ba, kamata yayi suyi ihu cikin murna amma sun tare ni da abunda zai juya min hankali
         “Muna maka magana dole kayi shiru tunda baka da abunda zaka ce, bayan kasan ba haka ango ke kasance wa ba a duk lokacin da akayi masa biki a garin nan” wadannan kuma kalaman dayan abokin nawa ne, tanimu, na kalle shi shima mamaki bai barni na bashi amsar su ba, har sai da alasan ya tabani tare da magana
         “Ya kayi mana shiru muna yi maka magana”
         “Ai mamaki kuke bani ne, dan naji kuna fadin wasu abubuwa da bansan da su ba” janaidu ya kalle ni yana rike da wukar dake hannunsa wadda yake niyyar yankan naman dan dandanawa
         “Haka kake dama ai jamilu, baka canzawa kuma ba zaka canza ba duk da auren nan da akayi maka! Ya dai kamata kasan mutum na sakewa a duk lokacin da akayi masa aure”
         Na tsaya ina kallon su kamar wani gaula saboda abun yana so ya bani dariya da kuma mamaki, janaidu ya sake yi min magana wannan karon a fusace
         “wai kai baka san mu bane ka zo ka tsaya sai kallon mu kake yi? Ko ko a wurin kamun zomon ka yi gamo da wani abu ne?”
         Na hadiye miyau sannan na kalle shi
         “ka dauka cewa duk maganganun da kake yi babu wanda nake ganewa a ciki, saboda ba kayi min su yadda zan gane ba janaidu, yaya zaku tare ni da wadannan kalamai gatsau gatsau dasu ba kai ba gindi? To idan ma wasa kuke yi zanso dan Allah ku janye dan ku barni da hutun gajiyar da na sha”
         Tanimu ya dan tsaya yana nazari na dan ya fisu hankali shi yana da saurin fahimta¸nasan shi zai fada min gaskiya ba zai yi min wasa ba
         “hmm! me kake so to mu fada maka da ya fi haka jamilu?”
         Na kalli tanimu shi janaidu tuni haushi yasa ya durkusa kasa ya bar mu yana gyaran naman kajin
         “Tanimu nasan zaka fahimce ni, dan haka kai ya kamata in fadawa gaskiya, yanzu fa na dawo daga tafiyar da nayi tun waccan shekarar da ta wuce yaya zaku tare ni da wadannan kalaman na wauta da basu dace ba, dan Allah ku fada min waye yayi aure a cikin ku?”
         A yanzu gaba dayan su suka dago suna kallo na, da wani irin kallo na mahaukaci, alasan dama mugun matsoraci ne, tuni ya ja da baya yana kallo na daga baya baya, janaidu ya kauda maganar fushi daga fuskar sa yana nazarina
         “Idan so kake mu nanata maka abunda kaima nasan ka sani shine, aurenka ake yi jamilu! Auren ka ake yi kai da masoyiyar ka!”
         Na dan yi kasake karo na barkatai ina kallon su, tabbas a yanayin su da gaske suke. Aure na ake yi kamar yadda suka fada
         Amma yaushe nace musu ina so?
Na numfasa cikin bacin rai
         “Dama har yanzu ba a daina auren kaka da kakanni ba janaidu?”
         Janaidu ya gyada kai
         “Ai ban san irin auren da kake magana ba jamilu”
         “Na dauka an daina aure ba tare da mutum yana nan ba, na dauka an daina aure ba tare da sanin ma’auratan ba..........”
         Alasan ya numfasa a dan tsorace har yanzu
         “To ai kai da saninka, kai da amincinka, tunda har ruwa sai da aka kai rana akan ka bari sai badi, amma kayi tsalle ka bidire akan dole sai an yi maka”
         Mamakina yanzu yana so ya nunku
         “Ban gane ba!”
         “Me kake so ka gane?” inji janaidu
         “Ni fa bani aka yi ma auren nan ba, wai baku yarda yanzu dawowa ta kenan daga birni bane?”
         Tanimu ya bani amsa da tambaya.
         “Wai baka yarda kai ne kayi auren nan bane jamilu? Ko ka fara taurin kai ne?”
         Janaidu ya kalle shi
         “Wannan ba taurin kai bane, rainin wayau ne, dan haka mu fasa maganar cin kajin nan muje mu raka jamilu dakin matar sa dan ya nuna mana alamun ya zaku da yawa ne”
         Suka kalle ni da gaske suke, ganin zasu maida ni mahaukaci yasa na daka musu tsawa cikin fushi da tada jijiyar wuya dan nima fa masifaffe ne idan naga za’a raina min wayau
         “Bana son iskanci da rashin hankali! Me ya same ku ne? kun sha kwaya ne janaidu!! Yaya zaku zo ku tirke ni ku na min maganganun da ban sa da su ba? Ni ban san wata amarya ba, hasalima ban san nayi aure ba,  gaba daya ma yanzunnan na dawo daga birni tun tafiyar da nayi shekarar bara da ta wuce, yaya zaku maida ni kamar na fita daga hayyaci na? haba ku natsu mana, ku fada min idan anyi min auren dole ne kuke jin nauyin fada min wallahi hankali na zai fi kwanciya akan kuna so ku maida ni wani shashasha
         Yanzu sun tabbatar da gaske nake, sun tabbatar da cewa watakila nayi gamo, na fahimci hakan ne ta hanyar wani kallo da suke yi min kana suka kalli junansu, alasan ya kalli tanimu
         “Shin wai tanimu! Da sanyi ne kadai aljanu suka fi saurin kama mutum?”
         Tanimu bai gane me yake nufi ba
         “Ban gane ba, me yasa ka tambaya?”
Ya nuna ni da hannu yana rawa
         “Da sai in ce tabbas jamilu gamo yayi da aljanu!”
Janaidu ya kalli alasan a fusace
         “Lallai kuwa da aljanin da ya kama ango a daren auren sa na farko da ya cika tsinannen aljani mara tausayi! Amma kuma ina ga kamar haka ne, kamar jamilu yayi gamo da mummunan aljanu masu birkida tunani”
         Raina ya baci sosai, na kalle su tare da nuna su da yatsa
         “Kada ku maida ni mahaukaci mana, alhalin kune mahaukata, kuna maganganun da ban san kansu ba, a gidan ubanwa aljani ya kamani?”
         Tanimu ya ce
         “Ai gani suka yi ka rikice ne, tare da kai fa muke tsaye a nan dazu, tare muka yanka kajin  nan, kuma tare muka fige su, duk ma ba wannan ba, kana nufin  duk  soyayyar da kuka yi da RUDA ba kai bane? Duk soyayyar da kuka shafe tsawon shekara daya da wasu watanni ba kai bane? Haba jamilu kuma sai mu yarda ba gamo kayi da aljanu ba?”
         I zuwa yanzu kaina ya fara ciwo, me wadannan suke so su fada min? me ke faruwa ne? yaushe na yi soyayya da wata mai suna RUDA? Yaushe na yi soyayya da ta kai tsawon shekara daya a nan garin? Na tabbata dai na taba yi amma a birni, amma a kaduna da naje nayi da masoyiya ta hajara ‘yar gidan da naje nake neman kudi a can? Amma ya zasu ce min haka?
         Na dukar da kai tare da dagowa na kalli tanimu
         “Ni dai na san ba ni bane, dan ni yanzu na dawo daga birni, dan haka duk inda zamu je a duniya sai dai muje zan tabbatar muku da kune kuka haukace, watakila kuma kune ma kuka yi gamo da aljanu. Ni kunga tafiya ta wahalar gajiya bata sake ni ba”
         Na juya kenan, janaidu ya kamo ni, na juyo tare da sa hannu na hankade shi yayi taga taga zai fadi, matsoraci alasan ya ja da baya da sauri yana shirin guduwa, tanimu ya dakatar da janaidu, janaidu ya kalle shi a fusace
         “Na rantse da kwarankwatsi! Nasha aradu nasha yasin! Sai ya zo munje dakin amaryar sa, yaya kuke so ya maida ku wawaye ne? kun manta da yadda angwaye a garin nan kunya ke sa su guduwa, ranar  farko? Dan haka yanzu ma jamilu so yake ya gudu da wayau washe gari a kira mu wawaye dan mun kasa kai ma amaryar sa shi”
         Suka kalli juna, alamun yarda suka zo musu, sannan suka fashe da dariya, alasan ya kalle ni
         “Amma anyi shakiyi jamilu! Ai bamu san haka bane gashi har ka tsorata mu wallai”

         Ina ji ina gani suka cukume ni tun ina tirjiyewa cike da hayaniya har suka kimkime ni suke yi cikin gida dani, sai da aka nufi dakin da naga anyi ma feshi da farar kasa irrin ta amare naji gaba na ya yanke yayi wata bahaguwar faduwa, sai lokacin tunanin wani abu yazo min a raina

AKWAI CI GABA....

Comments

Popular posts from this blog

YAR BARIKI babi na daya